in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya na neman bangarori masu zaman kansu su zuba jari a bangaren bunkasa wasanni
2018-06-08 13:03:59 cri

Gwamnatin Nijeriya, ta yi kira ga bangarori masu zaman kansu, su ci gajiyar kyakkyawan yanayin kasuwanci da ke akwai a kasar, don zuba jari a bangaren raya harkokin wasanni.

Ministan matasa da wasanni na kasar Solomon Dalung ne ya yi kiran jiya a Lagos, cibiyar harkokin kasuwancin kasar, inda ya ce, akwai bukatar bangarori masu zaman kansu a kasar su shiga a dama da su a bangaren, domin gano dimbim damarmakin dake kunshe cikin zuba jari a harkokin wasanni.

Solomon Dalung ya shaida wa manema labarai cewa, bangarori masu zaman kansu ne ke bunkasa harkokin wasanni a duniya, yana mai cewa, ba lallai ne a samu alfanu nan take ba, amma jari ne da idan ya habaka zai shafe lokaci mai tsawo. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China