Babban mashawarci na musamman na kasar Sin Wang Yang, zai gudanar da ziyarar aiki ta sada zumunta a kasashen Congo, da Uganda da Kenya tsakanin ranekun 11 zuwa 20 ga watan nan na Yuni.
Mr. Wang, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin ba da shawarwari na dandalin tattauna harkokin siyasa na kasar Sin, zai ziyarci kasashen ne bisa gayyatar shugaban majalissar dattijan kasar Congo Pierre Ngolo, da gwamnatin kasar Uganda, da kuma kakakin majalissar dokokin kasar Kenya Justin Muturi.(Saminu Alhassan)