in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan za ta shirya taro tsakanin shugaban kasar Sudan ta kudu da madugun 'yan tawayen kasar
2018-06-06 10:36:12 cri

Kasar Sudan ta gabatar da wani yunkuri na shirya taron ganawa tsakanin shugaban kasar Sudan ta kudu Salva Kiir, da madugun 'yan adawar kasar Riek Machar.

Ma'aikatar harkokin wajen Sudan ta bayyana cikin wata sanarwa jiya Talata, cewar wata babbar tawagar wakilai daga kasar Sudan ta ziyarci Juba a ranar Talata, inda ta gabatar da wasikar da shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ya aikewa takwaransa na Sudan ta kudu Salva Kiir.

A cewar sanarwar, tawagar wakilan ta kunshi ministan harkokin wajen kasar Sudan Al-Dirdiri Mohamed Ahmed, da ministan albarkatun mai da iskar gas na kasar Azhari Abdul-Ghader Abdullah, da kuma babban jami'in hukumar tattara bayanan sirri na kasar Sudan Salah Abdallah.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China