Al'ummomin Burkina Faso na sa ran samun moriya bisa maido da huldar diplomasiyya tsakanin Sin da kasarsu
Wang Yi, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, ya kulla yarjejeniyar maido da huldar diplomasiyya tsakanin Sin da kasar Burkina Faso, tare da takwaransa na kasar Burkina Faso, a ranar 26 ga wata, a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. Dangane da batun, al'ummomin kasar Burkina Faso masu sana'o'i daban daban sun nuna farin cikinsu, inda suke sa ran ganin maido da huldar diplomasiyya tsakanin Sin da Burkina Fason zata haifar musu da moriya. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku