in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar Amurka ta isa DPRK don shirya ganawar shugabannin kasashen biyu
2018-05-28 09:17:58 cri
Shugaba Donald Trump na Amurka ya tabbatar da cewa, wata tawagar jami'an kasar sun isa Koriya ta arewa(DPRK) a jiya Lahadi don tattaunawa game da shirye-shiryen ganawarsa da shugaba Kim Jong Un da aka shirya gudanarwa a ranar 12 ga watan Yuni a kasar Singapore.

Shugaba Trump ya sanar da hakan ne jiya Lahadi a shafinsa na Tweeter. Ya ce yana da imanin cewa,Koriya ta arewa tana da albarkatu, kuma wata rana za ta kasance babbar kasa a fannin tattalin arziki da harkokin kudi, kuma shugaba Kim Jong Un ya yarda da kalaman na Trump.

A jiya Lahadi ne dai jaridar Washington Post ta ba da labarin cewa, tsohon jakadan Amurka a Koriya ta Kudu Sung Kim ya tsallaka kasar Koriya ta arewa inda ya gana da mataimakin ministan harkokin wajen kasar Koriya ta arewan Choe Son Hui game da shirye-shiryen taron kolin shugabannin kasashen biyu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China