in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta kara zuba jari a bangaren ilmi, kamfanonin madara da ayyukan hidima
2018-05-24 09:59:03 cri
Majalisar kolin mulkin kasar Sin ta sanar da cewa gwamnatin Sin za ta kara zuba jari a fannin ilmi a yankunan da suke fama da fatara da kuma daukar matakan bunkasa kamfanonin samar da madara, tare da bada fifiko ga ci gaban ayyukan bada hidima.

A sanarwar da aka fitar bayan kammala zaman majalisar kolin kasar Sin wanda firaiministan kasar Li Keqiang ya jagoranta a jiya Laraba ta bayyana cewa, gwamnatin tsakiya za ta kara zuba kudi kimanin yuan biliyan 13, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 2 wajen samar da tallafi da koyar da ilmin sana'a a yankunan tsakiya da yammacin kasar Sin, wadanda suka fi fama da talauci.

Kasar Sin za ta karfafa bangaren kudadenta, da inshora, da kuma tallafawa bangaren kamfanonin samar da madara.

Majalisar kolin ta kasar Sin ta ce tana bukatar yin amfani da yankuna 17 a matsayin na gwaji ciki har da birnin Beijing, domin zurfafa shirinta na bunkasa ci gaban fasahohi da ayyukan bada hidima. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China