Cimma matsaya daya kan shawarwarin tattalin arziki da cinikayya ya dace da muradun kasashen Sin da Amurka
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya ce, yadda kasashen Sin da Amurka suka cimma matsaya daya kan shawarwarin tattalin arziki da cinikayya ya dace da muradun kasashen biyu. Lu ya bayyana haka ne a yayin taron manema labaru da aka shirya a yau Litinin, inda ya kara da cewa, kamata ya yi gwamnatocin kasashen biyu su sauke nauyin dake bisa wuyansu kan dukkan abubuwan dake amfanawa jama'ar kasashen biyu. (Bilkisu)