in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gabatar da sakamakon zaben 'yan majalisar dokokin kasar Iraki
2018-05-19 16:31:22 cri
Yau Asabar, kwamitin kula da harkokin zabe mai zaman kansa na kasar Iraki ya gabatar da sakamakon zaben 'yan majalisar dokokin kasar. Kawancen al-Sa'iroon dake karkashin shugabancin jagoran Shi'a Moqtada al-Sadr ta samu kujeru kimanin 54 daga cikin adadin kujeru 329 na majalisar dokokin kasar, wanda yake kan gaba a sauran kawancen da suka halarci zaben.

A bisa tsarin mulkin kasar Iraki, jam'iyyar da ta fi samun kujerun majalisar dokokin kasar tana da ikon nada firaministan kasar da kuma kafa gwamnati, kuma sabuwar kawancen da aka kafa bayan da aka gabatar da sakamakon zaben zai iya kasancewa a matsayin "babbar jam'iyya". (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China