in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sanar da murabus din Gwamnatin Guinea
2018-05-18 10:36:43 cri
Gwamnatin Guinea, waddda firaminsta Mamady Youla ke jagoranta, ta sanar da murabus dinta a jiya Alhamis, inda kasar dake yammacin Afrika, ke dakon sabuwar Gwamnati da za a kafa cikin raneku masu zuwa.

Ministan harkokin waje, kuma Sakatare janar na fadar shugaban kasar, Kiridi Naby Youssouf Bangoura ne ya sanar da matakin cikin wata sanarwa da ya fitar a hukumance.

Bangoura, ya ce shugaban kasar Alpha Conde, ya umarci Firaministan da Gwamnatin mai barin gado, su kula da harkokin yau da kullum har zuwa lokacin da sabuwar Gwamnati za ta fara aiki.

A watan Junairun 2016 ne, dokar musammam ta shugaban Jamhuriyar Guinea, ta kafa Gwamnatin mai barin gado, da ta kunshi ministoci 33, ciki har da sakatare janar 2. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China