Yau Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aika wa takwaransa na kasar Indonesia Joko Widodo sakon jaje, dangane da harin ta'addanci da ya auku a Indonesia.
A cikin sakonsa, shugaba Xi ya ce, kasar Sin na adawa da ko wane nau'in aiki na ta'addanci, tana kuma fatan hada kai da Indonesia, da sauran kasashen duniya, wajen yaki da 'yan ta'addda tare, a kokarin kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankuna da ma duniya baki daya. (Tasallah Yuan)