in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
EU ta tsawaita wa'adin shirinta na ba da horo a Mali
2018-05-15 10:38:54 cri

Tarayyar Turai EU, ta sanar da tsawaita wa'adin shirinta na ba da horo a Mali da shekaru biyu, inda zai kai ranar 18 ga watan Mayu 2020.

A cewar sanarwar da tarayyar ta fitar a jiya, majalisarta ta yanke shawarar tsawaita wa'adin ne, domin ya kunshi taimakawa rundunar hadin gwiwa ta kungiyar kasashe 5 na yankin Sahel.

Majalisar ta kuma amince da ware Euro miliyan 59.7 kwatankwacin dala miliyan 71.5 ga shirin a cikin shekarun biyu.

Shirin da aka kafa a shekarar 2013, na da nufin ba da taimako da horo ga sojojin Mali, tare da ba hukumomin kasar shawarwari kan sauya tsarin rundunarta na soji.

A shekarar 2014 ne, kasashen Burkina Faso da Chadi da Mali da Mauritania da kuma Niger, suka kafa kungiyar Sahel, domin inganta hadin gwiwa a yankin, da nufin magance manyan kalubalen da suke fuskanta. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China