Babban hafsan sojin kasa na Nijeriya Tukur Buratai, ya ba sojoji umarnin fatattakar bata gari daga yankin Birnin Gwarin jihar Kaduna mai fama da ayyukan bata gari cikin makonni 3.
Sama da fararen hula 100, ciki har da sojoji 11, 'yan bindiga suka kashe a kauyukan dake karamar hukumar Birnin Gwari, cikin watanni 5 da suka gabata.
Da yake kaddamar da wani sansanin soji a yankin Birnin Gwari, babban hafsan sojin, ya bukaci dakarun su tabbatar da kawo karshen kashe kashen da ake yi a yankin.
A cewarsa, ba za su sake tsayawa daukar matakan kariya ba, inda ya ce, dole ne a kaddamar da yaki. Ya ce, tun da bata garin na gudanar da ayyukansu, dole ne a mayar musu da martani kuma a murkushe su a duk inda suke. (Fa'iza Mustapha)