in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi ya bukaci a ingiza hadin gwiwa tsakanin babban yankin kasar da yankin Hong Kong don ci gaban kimiyya da fasaha
2018-05-14 15:28:51 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bukaci a kara karfafa hadin gwiwar dake tsakanin babban yankin kasar da yankin musamman na kasar Hong Kong domin raya ci gaban kimiyya da fasaha, inda ya lashi takobin tallafawa yankin don zama cibiyar bunkasa fasahar kirkire kirkire ta kasa da kasa, da kuma baiwa masana kimiyya na yankin damar ba da gudumowarsu wajen ci gaban kasa ta fannin kim'iyya da fasaha.

Xi, wanda kuma shi ne babban sakataren jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban kwamitin aikin sojin kasar Sin, ya ba da wannan muhimmin umarni ne a daidai lokacin da yake mai da martani dangane da wasikar da wasu 'yan kimiyya 24 dake yankin Hong Kong na kasar suka rubuta masa a watan Yunin shekarar 2017.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China