in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Trump: Amurka da Sin na kokarin ganin kamfanin ZTE ya dawo da harkokinsa
2018-05-14 10:16:20 cri
Shugaba Donald Trump na kasar Amurka ya bayyana cewa, kasarsa da Sin na kokarin ganin kamfanin ZTE na kasar Sin dake kera na'urorin sadarwa, ya dawo da harkokinsa, sakamakon haramcin fitar da hajojinsa da kasar Amurka ta kakaba masa.

Shugaba Trump wanda ya bayyana hakan a shafinsa na Tweeter, ya ce bangarorin biyu na kokarin ganin kamfanin ya ci gaba da gudanar da harkokinsa yadda ya kamata. Ya ce ya umarci ma'aikatar kasuwancin Amurkar da ta warware wannan matsala.

A tsakiyar watan Afrilun wannan shekara ce dai aka tilastawa kamfanin ZTE daya daga cikin manyan kamfanoni dake kera nau'rorin sadarwa a duniya dakatar da ayyukansu a duniya baki daya, bayan da ma'aikatar kasuwancin Amurka ta haramtawa kamfanonin kasar fitar da kayayyakin kamfanin.

Yanzu haka dai kamfani na ZTE yana tattaunawa da bangaroirin da wannan batu ya shafa don ganin an warware wannan batu, yana mai jaddada cewa, yana dora muhimmanci wajen martaba dokar hana fitar da nau'rorin da aka sanya masa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China