in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ceto bakin haure kimanin 260 a gabar tekun yammacin Libya
2018-05-14 09:36:07 cri

Masu tsaron gabar tekun Libya a ranar Lahadi sun yi nasarar ceton bakin haure ta barauniyar hanya kimanin 260 daga nahiyoyin Afrika da Asiya a yammacin gabar tekun Libya.

Kakakin dakarun tsaron ya ce, jami'an sun yi nasarar ceton bakin haure kimanin 180 da suka fito daga shiyyar Afrika da Asiya a cikin wasu kwale kwale na roba guda biyu a wani waje mai tazarar kilomita 36 daga birnin Garrabulli, wanda ke da nisan kilomita 60 daga Tripoli, babban birnin kasar, kakakin dakarun tsaron, Ayob Qassem ya tabbatar da hakan ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua.

Qassem ya kara da cewa, an kwashe wadanda aka ceto din zuwa sansanin sojojin ruwa dake Tripoli, kana an samar musu da tallafin jin kai da magunguna, sannan an mika su ga hukumar samar da matsugunai ta Tripoli a gaban wasu kungiyoyin kasa da kasa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China