A 'yan kwanakin nan ne ruwan sama kamar da bakin kwarya ya haddasa mummunan ambaliyar ruwa a kasar ta Somaliya, inda matsalar ta rutsa da mutane sama da dubu dari hudu.
Mista Geng ya bayyana cewa, kasar Sin na jajantawa dimbin mutanen da ambaliyar ruwar Somaliyar ta tilasta musu barin muhallansu. Gwamnatin kasar Sin za ci gaba ta sanya ido kan halin da ake ciki a Somaliya, da samar da tallafi da goyon-bayan da Somaliya take bukata daidai karfinta.(Murtala Zhang)