in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasashen Sin da Japan da Koriya ta kudu sun bayar da hadaddiyar sanarwa
2018-05-10 09:52:34 cri
A jiya Laraba, firaministan kasar Sin Li Keqiang, da takwaransa na kasar Japan Shinzo Abe, da kuma shugaban kasar Koriya ta kudu Moon Jae-in, suka yi taro karo na bakwai a tsakaninsu a birnin Tokyo, fadar mulkin kasar Japan, inda suka fitar da hadaddiyar sanarwa dongane da ganawa tsakanin shugabannin Koriya ta arewa da ta kudu a shekarar 2018.

Sanarwar ta jinjinawa gamayyar kasa da kasa, bisa kokarin da suka yi na ganin kyautatuwar yanayin da ake ciki a zirin Koriya. Shugabannin kasashen nan uku sun yi maraba da ganawar da shugabannin kasashen Koriya ta arewa da ta kudu suka yi a ranar 27 ga watan da ya wuce, kuma suna fatan sassa masu ruwa da tsaki za su ci gaba da kokari, musamman ma game da ganawar da ba da jimawa ba za a gudanar tsakanin shugabannin Koriya ta arewa da Amurka, tare da fatan za a daidaita matsalolin da ke jawo hankalin sassa daban daban, tare da kiyaye kwanciyar hankali a shiyyar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China