Firaministan Lesotho Thomas Thabane ya kawo karshen ziyarar aikinsa a Sudan a jiya 8 ga wata.
An ba da labarin cewa, yayin ziyarar tasa, kasashen biyu sun ba da wata sanarwa cikin hadin kai domin bayyana fatansu na hadin gwiwa wajen dakile ta'addanci da 'yan cin rani ba bisa doka ba da kuma aikata laifufuka a kasashen waje. Ban da wannan kuma, kasashen biyu na bayyana fatansu na kara habaka dangantakar dake tsakaninsu da kara hadin kai a wasu manyan fannoni ciki hadda siyasa, tattalin arziki, al'adu, al'umma, harkokin diflomasiyya da dai sauransu. (Amina Xu)