in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar Sojan Nigeria ta ceto mutane fiye da dubu daga hannun Boko Haram
2018-05-08 09:27:31 cri

Rundunar Sojan Nigeria, ta ce dakarunta sun gudanar da ayyukan ceto sau da dama a jihar Borno dake arewa maso gabashin Nigeria, inda suka kubutar da mutane kimanin dubu daya daga hannun kungiyar Boko Haram.

Kakakin rundunar ya ce, sojojin hadin gwiwa na Kamaru da Chadi da Niger da Nigeria ne suka gudanar da wadannan ayyuka a kwanakin baya.

Sojojin sun kuma harbe mambobi biyar na Boko Haram yayin ayyukan da suka gudanar cikin watan da ya gabata a jihar Borno, inda kuma suka ceto mutane 149.

Ban da wannan kuma, gwamnatin kasar ta kaddamar da ayyukan soja na dakile Boko Haram dake boye a jihar Borno sau da dama a bara. (Amina Xu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China