in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata kamfanonin waje a kasar Sin su girmama'yancin mallaka gami da cikakken yankin kasar Sin
2018-05-07 10:23:00 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mista Geng Shuang ya ce, ya zama dole kamfanonin kasashen waje dake aiki a kasar Sin, su girmama 'yancin mallakar yankin kasar, gami da cikakken ikonta.

A kwanakin baya ne, Amurka ta fitar da wata sanarwa, inda ta soki gwamnatin kasar Sin, saboda ta bukaci kamfanonin kasashen waje dake aiki a kasar, su kaucewa ayyana yankunan Hongkong da Macau a matsayin 'kasa' a shafukansu na Intanet gami da litattafansu na talla.

Game da zargin ne Mista Geng Shuang ya yi sharhi a jiya, yana mai cewa, duk abun da Amurka za ta fada, sam ba zai canja gaskiyar magana ba, wato kasancewar kasar Sin daya tak a duk fadin duniya, kana, Hongkong da Macau, yankuna ne da ba za'a iya balle su daga kasar Sin ba.

Geng ya kara da cewa, kasar Sin za ta ci gaba da raya dangantakar abota da sauran kasashen duniya, bisa manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Geng ya sake nanata cewa, kamata ya yi kamfanoin kasashen waje dake kasar Sin, su girmama cikakken yankin kasar, tare da mutunta dokokin kasar da al'ummarta baki daya. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China