in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manyan jami'ai masu kula da harkokin kudi na kasashen Sin, Japan da Koriya ta Kudu sun bukaci a yi yaki da ra'ayin kariyar cinikayya
2018-05-06 16:43:19 cri
An gudanar da taron ministocin kudi da shugabannin baitulmalin kasashen Sin da Japan da Koriya ta Kudu, ranar Jumma'ar da ta gabata a birnin Manila, hedkwatar kasar Philippines, inda manyan jami'ai mahalarta taron, suka yi musayar ra'ayi dangane da batutuwan da suka hada da yanayin tattalin arzikin kasashen 3, da hadin gwiwar da ake cikin yankinsu a fannin hada-hadar kudi. Jami'an sun yi kira da a yi kokarin yaki da ra'ayin kariyar cinikayya, don tabbatar da tsarin bude kofa a fannin huldar cinikayya dake tsakanin bangarori daban-daban.

Ban da haka, cikin sanarwar hadin gwiwa da aka gabatar bayan taron, an yi kira da a yi hattara wajen tunkarar matsalar da ka iya bullowa ta koma bayan tattalin arzikin duniya. Sanarwar ta kara da cewa, kowa ya lura da hadarin dake tare da matakan kariyar ciniki, inda kasashe daban daban ke daga matsayin ruwan da ake bayarwa bisa ajiyar kudi, sannan saurin karuwar kudin ruwa ya zarce yadda aka yi hasashe. Ban da haka kuma, ana ci gaba da fuskantar rikicin siyasa a wasu shiyyoyi.

Ganin yanayin da ake ciki, ya sa mahalarta taron jaddada kin amincewa da duk wani mataki irin na kariyar cinikayya, da bukatar bude kofa domin gudanar da ciniki da zuba jari, da karfafa musayar ra'ayin da ake yi tsakanin kasashen Sin, Japan da Koriya ta Kudu.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China