in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha: Ficewar Amurka daga yarjejeniyar nukiliyar Iran zai haddasa illa ga tsarin hana yaduwar makaman nukiliya
2018-05-04 10:19:38 cri
Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergei Lavrov ya bayyana cewa, idan kasar Amurka ta fice daga yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran, hakan zai haddasa illa ga matakan hana yaduwar makaman nukiliya a duniya

Mr. Lavrov ya bayyana haka ne bayan ganawarsa da takwaransa na kasar Jordan Ayman Safadi a birnin Sochi na kasar Rasha, yana mai cewa, idan kasar Amurka ta fice daga yarjejeniyar, kamar yadda shugaban kasar Donald Trump ya jaddada, gamayyar kasa da kasa za su rasa wata muhimmiyar yarjejeniya game da hana yaduwar makaman nukiliya a duniya.

Bugu da kari, ya ce, mai yiyuwa ne, takardun da Isra'ila ta gabatar a kwanan baya game da batun nukiliyar kasar Iran tsoffi ne, saboda a halin yanzu hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa na sa-ido kan dukkan ayyukan da suka shafi nukiliyar kasar Iran.

A daren ranar 30 ga watan Afrilu da ya gabata ne, firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya shaidawa taron maneman labarai cewa, hukumar leken asirin Isra'ila ta samu wasu takardu na sirri daga kasar Iran, inda take zargin kasar Iran da ci gaba da shirinta na kera makaman nukiliya, sabanin yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran da aka kulla. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China