in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren MDD ya yi Allah wadai da mummunan tashin hankalin da ya tashi a CAR
2018-05-04 09:18:47 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi Allah wadai da tashin hankalin da ya barke a Jamhuriyar Afirka ta tsakiya (CAR) har ma ya haddasa mutuwar mutane a kalla 22 kana sama da mutane 100 suka jikkata, baya ga wasu ma'aikatan da ake aikin wanzar da zaman lafiya a kasar karkashin laimar MDD (MINUSCA) guda biyu

Mataimakin kakakin MDD Farhan Haq ya ruwaito Guterres yana mika sakon ta'aziya ga iyalan wadanda tashin hankalin na ranar Talata ya shafa, tare da fatan samun sauki cikin gaggawa ga wadanda suka jikkata.

Guterres ya kuma yi kira ga hukumomi da su gudanar da bincike don gano wadanda ke da hannu a hare-haren don su gurfana a gaban kuliya, yana mai cewa bai ga dalilin tayar da rikici ko furta wasu kalaman nuna kiyayya ba.

A don haka ya sake nanata kudurinsa na goyon bayan gwamnatin kasar da ma matakan da tawagar ta MINUSCA ke dauka wajen kare rayukan fararen hula da samar da zaman lafiya a kasar. Ya kuma yi kira ga masu ruwa da tsaki da su hada kai don kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China