in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tunisia: An bude sashen samar da maganin cutar daji mafi girma a Afirka
2018-05-01 15:57:08 cri
Mahukuntan kasar Tunisia sun bayyana kaddamar da cibiyar samar da maganin cutar daji ko Cancer mafi girma a Afirka da gabas ta tsakiya a kasar.

Da yake karin haske game da hakan, shugaban cibiyar Lassaad Boujebal, ya ce bude wannan cibiya zai samar wa kasar Tunisia damar shigo da jari, wanda ya kai kusan dalar Amurka miliyan 20.47, tare da guraben ayyukan yi 100, da suka hada da likitoci da masana a fannin harhada magunguna.

Lassaad Boujebal, ya ce cibiyar na kunshe da dakin harhada magunguna na sarrafa maganin cutar daji da ma sauran cututtuka.

A nasa bangare kuwa, firaministan kasar Youssef Chahed, cewa ya yi kasar sa, na fatan biyan bukatun al'ummar ta, game da samar da magunguna na gida da kaso 60 bisa dari nan da shekarar 2020, adadin da zai haura kaso 51 bisa dari da kasar ke da shi a shekarar 2016.

Youssef Chahed ya ce sashen masana'antun harhada magunguna na Tunisia, na fatan samar da kudaden jarin da yawan su zai kai dala biliyan 1.35 nan da shekarar 2020.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China