in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An shirya taron shawo kan matsalar bakin haure a Libya
2018-04-26 11:07:24 cri

Ma'aikatar harkokin wajen kasar Libiya ta shirya taro na 3, game da tattauna kan batun kwararar bakin haure ba bisa ka'ida ba. Taron da ya gudana gaban manyan jami'ai, ciki hadda wakilan hukumomin kasa da kasa, da jakadun kasashen ketare dake aiki a Libiyan, tare kuma da wakilan shirin wanzar da zaman lafiya na MDD a kasar

Wata sanarwa da aka fitar bayan taron, ta bayyana cewa mahalartansa, sun saurari sassan da kasar Libiya ke baiwa fifiko game da bukatar tallafin kasa da kasa a fannin shige da fice. Sun kuma nazarci dabarun da ake amfani da su a yanzu haka, da yadda za a gwama su da manufofin da ake aiwatarwa a yanzu, duka dai da nufin shawo kan kalubalen da kasar ke ci gaba da fuskanta.

Sanarwar ta kara da cewa, wasu daga muhimman kudurori da aka zayyana, sun hada da tsarin ci gaban kasar, da dabarun dakile kwararar 'yan ci rani da safarar bil Adama.

Har wa yau an yi musayar yawu game da bukatun manyan biranen Libiya, da bukatar shigar masu zuba jari a fannin inganta noma a kudancin kasar, a matsayin hanyoyin magance kalubalen 'yan ci rani da kasar ke fuskanta.

Ma'aikatar kwadago ta kasar Libiya na kokarin magance wasu daga wadannan kalubale, inda take maida hankali sosai ga samar da damammaki, da dabarun samarwa jama'a sana'o'i a cikin kasar.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China