in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Israila ta dakatar da tusa keyar masu neman mafaka
2018-04-25 12:33:27 cri
Gwamnatin Isra'ila ta soke kudurin ta, na tuka keyar dubban masu neman mafaka 'yan kasashen Afirka dake yankunan ta, maimakon hakan mai yiwuwa ta tsare su a gidajen yari na musamman da aka tanada. Wannan mataki dai ya biyo bayan umarnin kotun kolin kasar ne, wanda ya hana mahukunta aiwatar da korar masu neman mafakar.

Gwamnatin kasar ta bayyana ta cikin wata sanarwa cewa, korar masu neman mafakar ba zabi ba ne a wannan gaba, musamman game da 'yan ci ranin kasashen Uganda ko Rwanda dake cikin yankunan Isra'ilan.

Alkaluman da ma'aikatar cikin gidan kasar ta fitar sun nuna cewa, akwai masu neman mafaka kusan 42,000 'yan asalin kasashen Afirka dake zaune a kasar, wadanda da daman su ke zaune a yankunan marasa galihu dake kudancin birnin Tel Aviv.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China