Kwamitin dake lura da harkokin cikin gida na kasar Afirka ta kudu, wanda aka dorawa alhakin bincikar matsayin kasancewa 'yan kasa, ga iyalan nan mawadata na gidan Gupta, ya amince da wasu sharrudda na gudanar da aikin sa.
An dai bude binciken ne, biyowa bayan umarnin da shugabar kwamitocin majalissar dokokin kasar Cedric Frolick ta bayar, game da alakar iyanan na Gupta da ma'aikatu daban daban na kasar. Da kuma yadda suka samu matsayin kasancewa 'yan Afirka ta kudu.(Saminu Alhassan)