in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kawar da iyakar mallakar hannayen jari ga kamfanonin waje a masana'antun kera ababen hawa
2018-04-17 19:26:36 cri

Mahukuntan kasar Sin sun bayyana aniyar aiwatar da wata sabuwar manufa, wadda za ta baiwa kamfanonin kasashen waje damar zuba jari a masana'antun kera nau'o'in motoci daban daban.

Wani babban jami'in hukumar tsara manufofin ci gaba da aiwatar da sauye sauye ta Sin ne ya bayyana hakan a Talatar nan, yana mai cewa masu zuba jari na ketare, za su iya mallakar hannayen jari a fannin kera motoci na musamman, da wadanda ke amfani da makamashin da ake iya sabuntawa nan gaba cikin wannan shekara ta 2018.

Kaza lika za a samar da wannan dama ga masu zuba jari a fannin kirar motocin da daidaikun mutane ke saya daga shekarar 2020, da kuma motocin amfanin al'umma da yawa a shekarar 2022.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China