Ma'aikatar kasuwanci ta kasar Sin ta fitar da wata sanarwa a yau Talata, inda ta gabatar da sakamakon binciken da aka yi kan jibge dawar da Amurka ke yi a kasar. Ma'aikatar ta ce, Amurka ta na jibge dawarta a kasar Sin, matakin da ya kawo babbar illa ga sha'anin samar da dawa a kasar Sin, abun da ya sa ta yanke shawarar daukar matakin hana jibge dawa na wucin gadi kan Amurka. (Amina Xu)