in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta dauki duk wani matakin da ya wajaba don kiyaye halaltaccen hakkin kamfanoninta
2018-04-17 11:25:49 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar kasuwancin kasar Sin, ya maida martani game da matakan da ma'aikatar kasuwancin Amurka ta sanar na cewa, za ta haramtawa kamfanin sadarwa na kasar Sin wato ZTE sayo kayayyaki daga wajenta, inda ya ce kasar Sin za ta sa ido sosai kan wannan batu, kana, a shirye take wajen daukar duk wani matakin da ake bukata, don kiyaye hakokkin kamfanoninta.

Mai magana da yawun ma'aikatar ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin na bukatar kamfanoninta dake kasashen waje su bi dokokin kasashen da suke, da gudanar da cinikayya bisa doka. Kamfanin sadarwa na ZTE na hadin-gwiwa da kamfanonin Amurka sama da dari a fannonin da suka shafi zuba jari da cinikayya, da bayar da gudummawar dubun-dubatar guraben ayyukan yi a Amurka. Sin na fatan Amurka za ta daidaita wannan sabani bisa doka, tare da kokarin samarwa kamfanonin kasar Sin wani kyakkyawan yanayin kasuwanci cikin adalci kuma bisa doka da oda. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China