in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: ba za a samu daidaita rikicin Syria ta matakin soja ba
2018-04-16 20:39:10 cri
Dangane da batun kai hari ga kasar Syria da kasashen Amurka, Birtaniya, da Faransa suka yi da makamai masu linzami, mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Madam Hua Chunying ta ce, yadda ake dogaro kan matakan soja zai tsananta yanayin da ake ciki a yankin, da sanya maganar Syria ta kara zama mai sarkakiya da wuyar warwarewa. Saboda haka, kamata ya yi, masu ruwa da tsaki su lura da irin wannan batu da ya taba faruwa a baya, domin magance sake aukuwar kuskuren.

Madam Hua ta fadi haka ne a yau Litinin, a wajen taron manema labaru da aka saba da yi. A cewarta, yadda kasashen 3 suke kai hari ga kasar Syria ya sabawa tanadin dokokin kasa da kasa, na haramta yin amfani da karfin soja, haka kuma matakin da suka dauka, ya sabawa babban kundin tsarin MDD.

Kakakin kasar Sin ta kara da cewa, jami'an kasashen 3 sun ce "mai yiwuwa ne" gwamnatin kasar Syria ta yi amfani da makamai masu guba, sa'an nan suna "kokarin neman shaidu". Duk da cewa ba a tabbatar da ainihin abun da ya faru ba tukuna, an dora laifi kan wata gwamnati, gami da kai mata hari kai tsaye. Hakan a ganin kasar Sin, ba wani mataki na daukar nauyi ba ne.

Jami'ar kasar Sin ta kara da cewa, kasar Sin na adawa da amfani da makamai masu guba, bisa ko wane irin dalili. Kuma ta bukaci a yi cikakken bincike kan batun makamai masu guba na kasar Syria, don gano ainihin abun da ya faru.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China