in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU da MDD sun lashi tokobin karfafa hadin gwiwa wajen dawo da zaman lafiya a Jamhuriyar Afrika ta tsakiya
2018-04-14 13:05:05 cri
Tarayyar Afrika AU da MDD,sun jadadda kudurinsu na kara karfafa hadin gwiwa wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jamhuriyar Afrika ta tsakiya, tare da kare al'ummar kasar daga masu aikata laifuka.

Cikin wata sanarwar hadin gwiwa da aka fitar a Hedkwatar AU dake birnin Addis Ababa na Habasha, Kwamishinan kwamitin sulhu na AU Isma'il Chergui da mataimakin Sakatare Janar na MDD kan ayyukan wanzar da zaman lafiya Jean-Pierre Lacroix, sun bayyana damuwa game da ci gaban rikici a yankunan PK5 dake makwabtaka da Bangui babban birnin Jamhuriyar Afrika ta tsakiya.

Jami'an biyu, sun kai ziyarar yinin uku birnin Bangui, daga ranar 10 zuwa 12 ga wannan watan, inda suka tattauna da jami'an gwamnati da wakilan kungiyoyin al'umma da kungiyoyin mata da shugabannin addini da sauransu.

Sun kuma yi ta'aziyyar asarar rayuka da aka yi, ciki har da jami'an wanzar da zaman lafiya na kawance wato (MINUSCA), yayin wani samame da jami'an da hadin gwiwar jami'an tsaron kasar suka kai ranar 8 ga wata, a wani yunkuri na kawo karshen ayyukan bata garin dake barazana ga rayuwar al'umma a yankin Pk5 dake makwabtaka da Bangui,wadda kuma ita ce cibiyar tattalin arzikin birnin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China