in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manufar kasar Sin ta bude kofa da gyare gyare ta karfafa gwiwar Afirka ta fuskar yiwuwar samun ci gaba, in ji wani kusa a gwamnatin Kenya
2018-04-12 20:39:31 cri
Babban sakataren jami'iyyar Jubilee mai mulki a Kenya, kuma ministan wakilci a kasar Raphael Tuju, ya ce nasarorin da kasar Sin ta samu cikin 'yan shekarun baya bayan nan, sakamakon aiwatar da gyare gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen ketare, suna da matukar muhimmanci ga kasashen dake nahiyar Afirka, duba da cewa hakan na baiwa kasashen nahiyar wani karfin gwiwa na yiwuwar samun ci gaba.

Mr. Tuju wanda ya bayyana hakan a ranar Laraba, yayin zantawar sa da kamfanin dallancin labarai na Xinhua, ya ce nahiyar Afirka na fuskantar dumbin matsaloli, amma duk da haka, nasarorin da Sin ta cimma sun zamo darasi ga nahiyar, game da aiwatar da dabarun samun bunkasa.

Ya ce aiwatar da gyare gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen ketare, cikin shekaru 40 da kasar Sin ta sashe tana yi, su ne suka ba ta damar zamowa kasa ta 2 mafi karfin tattalin arziki a duniya, kuma ta daya a jerin kasashe dake tallafawa ci gaban tattalin arzikin duniyar baki daya.

A daidai wannan lokaci da kasar ke cika shekaru 40 da fara aiwatar da gyare gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen ketare, Sin za ta ci gaba da fadada kasuwannin ta, za ta kuma kara samar da damammaki na zuba jari, da karfafa kiyaye ikon mallakar fasaha, tare kuma da bullo da dabarun fadada shigo da kayayyaki.

Jami'in ya kara da cewa, abu ne mai matukar muhimmanci Sin ta kara fadada bude kofofin ta na kasuwanci. Wadannan matakai za su tabbatar da wanzuwar hada hadar cinikayya tsakanin ta da sauran kasashen dake nahiyar Afirka bisa salo na cudanya tsakanin sassan biyu. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China