in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci kasashen Afrika su gaggauta sakarwa matakan gwamnati mara don cimma ci gaba mai dorewa
2018-04-11 11:09:42 cri

Kungiyar kananan hukumomi ta nahiyar Afrika ta bukaci kasashen nahiyar su daukaka tsarin sakarwa matakan gwamnati mara don ba nahiyar damar cimma muradun ci gaba masu dorewa.

Sakatare janar na hadaddiyar kungiyar birane da kananan hukumomi ta Afrika Jean Pierre Elon Mbassi, ya bayyana wa Xinhua cewa, sakarwa matakan gwamnati mara zai taimaka wajen kai muhimman ayyuka kamar na kiwon lafiya da ilimi kusa da al'umma.

Sakatare janar din ya bayyana haka ne yayin taron kungiyar na yankin gabashin Afrika, inda ya ce, ya kamata ba matakan gwamnati iko ya zama abun da gwamnatocin Afrika suka sanya gaba, domin zai taimaka wa nahiyar cimma akasarin muradun ci gaba masu dorewa da take burin samun.

Taron na yini biyu ya mai da hankali ne kan nazarin nasarorin da aka samu game da ba matakan gwamnati iko a Afrika. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China