in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kara bude kofa ga kasashen waje da kasar Sin za ta yi zai kara habaka tattalin arzikin duniya
2018-04-10 19:37:35 cri
A yau Talata yayin bikin kaddamar da taron shekara-shekara na dandalin tattaunawa na kasashen Asiya na Boao, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani muhimmin jawabi, inda ya sanar da cewa kasarsa za ta dauki wasu sabbin matakai, na fadada bude kofarta ga kasashen ketare.

Game da hakan, mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana cewa, matakan da kasar ta dauka, sun taimaka matuka ga habakar cinikayya, gami da ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya.

Muhimman matakan da shugaba Xi ya sanar, sun nuna cewa, ci gaban da kasar Sin ta samu ya zama babban zarafi ga duk duniya, abun da kowace kasa za ta iya cin alfanunsa.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China