in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD ta yi alkawarin magance matsalar karancin abinci da 'yan gudun hijira ke fuskanta a Rwanda
2018-04-09 10:37:15 cri
Shugaban hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD UNHCR Flippo Grandi, ya yi alkawarin lalubo hanyoyin magance matsalar karancin abinci da 'yan gudun hijirar Congo ke fuskanta a Rwanda, ta hanyar tuntubar sauran hukumomi abokan hulda.

Da yake zantawa da manema labarai bayan ya ziyarci sansanin 'yan gudun hijira ta Gihembe dake lardin Gicumba dake arewacin Rwanda, Flippo Grandi ya ce za su gwada sabbin dabaru, inda za su tuntubi shirin samar da abinci na duniya game da neman taimako.

Ya ce akwai bukatar a kara karfafawa kokarin gwamnatin Rwanda na taiamkawa 'yan gudun hijira, yana mai cewa akwai bukatar ba 'yan gudun hijirar damar yin aiki da sauran hidimomi.

A cewar hukumar tunkarar annoba da kula da harkokin 'yan gudun hijira ta Rwanda, sansanin Gihembe na bada mafaka ga 'yan gudun hijirar kasar Congo kimanin 12,000.

Minista mai kula da hukumar Jeanne d'Arc de Bonheur, ya ce samun dawwaumammiyar mafita ya dogara ne ga karfafawa 'yan gudun hijirar ta yadda za su iya kula da kansu, ta hanyar horar da su fasahohi don kirkiro ayyukan yi, zuwa lokacin da za a samu zaman lafiya a kasarsu ta Jamhuriyar Demokradiyyar Congo. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China