in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ruftawar wani ramin hakar Gwal a Ghana ya yi sanadin mutuwar mutane 6
2018-04-09 10:02:54 cri
Mutane 6 sun mutu a ranar Asabar da ta gabata, lokacin da ramin hakar ma'adinan zinare ya rufta da su, a daya daga cikin wuraren hakar zinare na kamfanin Newmont dake Ghana.

Kamfanin ya tabbatarwa kafafen yada labarai na kasar cewa, al'amarin ya auku ne bayan ramin ya rufta a wani wurin da kamfanin ke aikin hakar ma'adinai a yankin Ahafo, dake da nisan kilomita 307 daga arewa masu yammacin birnin Accra.

Wata sanarwar da Newmont, kamfanin mafi girma na biyu wajen hakar zinare a duniya ya fitar, ta ce Mutane 8 ne ke aiki cikin ramin a lokacin da ya rufta

Wadanda suka mutun ma'aikata ne na kamfanin Consar da aka ba kwangilar gina saman ramin hakar zinare din da ya rufta.

An kwashe sauran ma'aikatan da suke wurin, tare da dakatar da aikin har zuwa lokacin da Newmont ya gamsu cewa za a iya fara aiki ba tare da wata matsala ba.

Tuni hukumomi suka fara bincike kan lamarin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China