in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Har kullum kasar Sin na bukatar kamfanoninta dake ketare su rika kiyaye dokokin kasashen waje
2018-04-04 19:14:09 cri

Yau Laraba ne kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya bayyana a yayin taron manema labaru a nan Beijing cewa, har kullum gwamnatin kasar Sin na bukatar kamfanonin kasar dake ketare, su rika bin dokokin kasashen da suke hada-hada, kuma rika sada mazauna wurin da alherai, a kokarin samun moriyar juna da nasara tare.

Mr. Geng ya ce kasar Sin na fatan yin kokari da kasar Mozambique, wajen ci gaba da raya huldar da ke tsakanin kasashen 2 yadda ya kamata.

Kwanan baya, hukumar Amnesty International ta kaddamar da wani rahoto dake cewa, wani kamfanin kasar Sin da aiki a Mozambique, ya gaza wajen kare muhalli kamar yadda dokokin wurin suka bukata, wanda hakan ya haddasa gurbatar muhallin wurin, tare da haifar da illa ga zaman rayuwar mazauwn wurin. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China