A wata sanarwa da mayakan suka fitar ta kafar yada labarai mai nasaba da kungiyar sun sanar cewa, sune suka hallaka Hassan Indha-Dhuh da Mohamud Moallim Hassan Fagase wadanda manyan jami'ai ne a gundumar mulki ta Hamarweyne dake yankin Banadir.
'Yan sandan Somali sun tabbatar da mutuwar jami'an biyu, sai dai sun ce ana cigaba da gudanar da bincike domin zakulo maharan wadanda suka tsere daga wajen bayan da suka kaddamar da harin.
A wani labarin kuma, dakarun wanzar da tsaro na kungiyar tarayyar Afrika sun dakile wani harin da kungiyar Al-Shabaab ta yi yunkurin kaddamarwa a wani sansanin soja da ke kudancin Somalia a ranar Lahadi.