in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Palastinawa sun gudanar da yajin aikin gama gari don juyayin wadanda suka mutu a zirin Gaza
2018-04-01 12:12:54 cri
Yankin yamma da kogin Jordan da zirin Gaza sun fuskanci yajin aikin gama gari a ranar Asabar don nuna juyayin kisan Palasnitawa 15 da Israila ta yi ta hanyar harbin bindiga a lokacin wani gangami da Palastinawa suka kaddamar a Gaza a ranar Jumma'a.

Yajin aikin ya kunshi na hada hadar kasuwanci, da bankuna, makarantu, jami'o'i da hukumomin gwamnati a zirin Gaza da yammacin kogin Jordan.

A kalla Palastinawa 15 ne aka hallaka, kana sama da 1,200 kuma suka jikkata a ranar Jumma'a a lokacin da dakarun Isra'ila suka bude wuta kan dandanzon Palastinawa wadanda ke gangamin ranar tunawa da kasarsu wanda suka gudanar a kan iyakar Gaza da Isra'ila.

Shugaban Palastinu Mahmud Abbas ya dora alhakin faruwar lamarin kan Isra'ila, kana ya ayyana ranar Asabar a matsayin ranar makoki ta kasa baki daya.

A wata sanarwar da ofishin firaministan Palastinu Rami Hamdallah ya fitar, ya bukaci kasa da kasa da su kawo karshen takaddamar dake tsakanin bangarorin biyu, yayin da babban batun dake zama jigo shi ne matsalar 'yan gudun hijira, bisa ga yarjejeniyar MDD mai lamba 194 da kuma batun kafa kasar Palastinu mai hedkwata a gabashin birnin Kudus. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China