in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana maraba da yin shawarwari a tsakanin Koriya ta Arewa da Koriya ta Kudu, in ji ma'aikatar harkokin wajen Sin
2018-03-29 19:45:46 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yau Alhamis cewa, kasar Sin ta yi maraba kwarai da gaske, bisa shirin gudanar shawarwari tsakanin kasar Koriya ta Arewa da takwararta ta Kudu, yayin zaman tattaunawar da ya gudana a birnin Panmunjom a yau din nan.

Lu Kang, ya kuma yi kira ga gamayyar kasa da kasa da su nuna goyon baya ga bangarorin biyu, ta yadda za su kyautata dangantakar dake tsakaninsu, da kuma ciyar da shawarwarin neman sulhu a tsakaninsu gaba.

Bisa labarin da aka samu, an ce, cikin shawarwarin da bangarorin biyu suka yi a yau Alhamis, sun tsai da kudurin ganawa a tsakanin shugabannin kasashen biyu a Gidan Zaman Lafiya dake birnin Panmunjom a ranar 27 ga watan Afrilu mai zuwa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China