Yang Jiechi zai kai ziyara kasar Koriya ta Kudu
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya sanar a yau 28 ga wata cewa, bisa gayyatar da gwamnatin kasar Koriya ta Kudu ta yi masa, wakilin musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping, kuma mamban hukumar siyasa ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban ofishin kwamitin kula da harkokin waje na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta Sin Yang Jiechi, zai kai ziyara kasar Koriya ta Kudu, tsakanin ranekun 29 zuwa 30 ga wannan wata. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku