in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar sin za ta inganta hakkokin ma'aikata masu basira
2018-03-27 11:24:28 cri
Kasar Sin ta fara shirin kara kaimi wajen inganta hakkokin ma'aikata masu basira, a daidai lokacin da kasar mai karfin tattalin arziki na 2 a duniya ke kokarin bunkasa ingancin ma'aikatanta don saukaka mata samun ci gaba.

Hukumomin tsakiya na kasar sun fitar da wasu tsare-tsare da za su bunkasa kudin shiga da matsayin ma'aikata masu basira.

Za kuma a karfafa gwiwar gudanar da sana'o'i don kara jan hankalin ma'aikata, ciki har da ba su karfin fada a ji a harkokin gudanar da ma'aikatu da albashi mai tsoka da damar sayen hannayen jari. Gwamnati za ta kuma ba ma'aikatan lakabi na alfarma tare da ba su kulawa ta musamman a fannonin samun gidaje da ilimin yaransu.

Kasar Sin na fatan dabarun za su ba ma'aikata kwarin gwiwar inganta basirarsu da kirkiro abubuwa ta yadda za su ja hankalin matasa masu basira zuwa ga ayyukan hannun wadanda suka shafi harhada abubuwa da gyare-gyare da gine-gine da sauransu.

A cewar mataimakin ministan kula da harkoki da tsaron al'umma na kasar Tang Tao, wannan ne karon farko da kasar Sin ta bada gagarumin muhimmanci kan wannan batu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China