in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Isra'ila ta ce ba a harba rokoki ba a yankunanta
2018-03-26 10:43:53 cri
Rundunar sojin Isra'ila ta ce hare-haren da suka fada kan cibiyar kakkabo makaman rokarta a daren Lahadi hakan ya faru ne ba da nufin kaddamar da hare-haren rokoki ba sai dai sakamakon harbe-harbe da manyan bindigogi a zirin Gaza.

Tun da farko a daren Lahadi, an yi ta jin karar jiniya a wasu birane da dama dake kudancin Isra'ila, kuma kakakin rundunar sojan ya samar da cewa cibiyar kakkabo makaman rokar ta kakkabo rokoki da dama da aka harba daga zirin Gaza zuwa Isra'ila.

Daga bisani an gano cewa babu wasu makamai da aka harba a yankunan Yahudawan da kuma cibiyar kakkabo makaman rokar wadanda aka harba daga yankuna dake karkashin ikon Palastinawa.

Wannan bude wutar wani bangare ne na rawar dajin da dakarun sojojin kungiyar Hamas, kungiyar fafutukar Palastinawa mafi girma dake zirin Gaza ta gudanar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China