Donald Trump ya sanar da nada John Bolton a matsayin mataimakin shugaba mai kula da harkokin tsaron kasar
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar a jiya cewa, John Bolton, tsohon zaunannen wakilin kasar a MDD, zai maye gurbin Herbert Raymond McMaster a matsayin mataimakin shugaba mai kula da harkokin tsaron kasar, inda zai fara aiki a hukumance a ranar 9 ga watan Afrilu mai zuwa.
An haifi John Bolton ne a shekarar 1948, kuma ya taba kasancewa zaunannen wakilin Amurka a MDD daga shekarar 2005 zuwa shekarar 2006. (Maryam)