in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Cutar kwalara ta hallaka 'yan ci ranin janhuriyar dimokaradiyyar Congo 36 a Uganda
2018-03-22 20:53:58 cri
Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta ce a kalla 'yan gudun hijirar kasar jamhuriyar dimokaradiyyar Congo 36 ne suka rasa rayukan su cikin watan Fabarairun da ya gabata, sakamakon kamuwa da cutar amai da gudawa ko Kwalara, a wani sansani na 'yan gudun hijira dake yammacin kasar Uganda.

Cikin wata sanarwa da ofishin WHO ya fitar, an bayyana cewa ma'aikatar lafiya, da gwamnatocin gundumomin kasar ta Uganda, na aiki tare da hukuma mai lura da 'yan gudun hijira ta MDD, da kuma asusun gaggawa na tallafawa kananan yara na MDD, da hukumar WHO, da kungiyar ba da agajin jin kai ta Red Cross mai aiki a Uganda, da sauran abokan hulda, domin tallafawa 'yan gudun hijirar.

A kalla 'yan gudun hira 50,000 ne daga lardin Ituri na jamhuriyar dimokaradiyyar Congo, ke neman mafaka a kasar Uganda a wannan shekarar kadai, tun bayan barkewar tashin hankali a ranar 17 ga watan Disambar bara.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China