in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ta yi kira ga Birtaniya don gudanar da bincike na hadin gwiwa kan yadda wani tsohon dan leken asirin kasar ya sha guba
2018-03-22 11:18:01 cri
Sashen hana bazuwar makamai da sa ido na ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha ya gabatar da wani bayani a jiya Laraba cewa, kasar Rasha na fatan ganin Birtaniya za ta nuna mata dukkan bayanan da ta samu dangane da yadda wani tsohon dan leken asirin kasar Rasha mai suna Sergei Skripal da diyarsa suka sha guba a kasar Birtaniya. Rasha ta ce a shirye take don gudanar da bincike na hadin gwiwa tare da Birtaniyar.

A jiya Laraba, ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta kira wani taro na musamman domin bayyana yanayin da ake ciki wajen bin bahasin batun, inda ta gayyaci wasu jami'an diplomasiyya na kasashen waje dake kasar Rasha. Bangaren Rasha ya ce, sai an ba shi damar gudanar da bincike kan lamarin, kafin ya iya samun damar gabatar da wani sakamako. Haka kuma, ya nanata cewa, ba shi da hannu a cikin batun, tun da lamarin ba zai taimaka wajen karfafa tsaron kasar Rasha ba.

Kafin haka, fadar shugabancin kasar Amurka ta "White House" ta gabatar da wani bayani a jiya Laraba cewa, shugaban kasar Donald Trump ya riga ya buga waya ga takwaransa na kasar Faransa, Emmanuel Macron, inda suka tattauna wajibcin tilastawa kasar Rasha daukar nauyin wannan batu, kuma sun nuna niyyar rufa wa kasar Birtaniya baya.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China