in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sudan ya tafi Kigali don halarta taron AU kan yankin ciniki mara shinge
2018-03-21 10:51:01 cri
Kamfanin dillancin labarai na kasar Sudan SUNA, ya ce Shugaban kasar Omar al-Bashir, ya tafi Kigali babban birnin Rwanda don halartar taro karo na 10 na Tarayyar Afrika AU, kan samar da yankin ciniki cikin 'yanci.

SUNA ya ruwaito cewa Shugaban Al-Bashir na jagorantar wakilan kasarsa zuwa taron na AU da aka amince da gudanar da shi yayin taron da Tarayyar ta yi a birnin Addis Ababa na Ethiopia cikin watan Junairun da ya gabata.

An fara taron ne a jiya Talata, inda za a kammala a yau Laraba.

Yankin ciniki mara shinge na nahiyar na da nufin zurfafa hadin kan tattalin arzikin nahiyar da inganta harkar noma da wadatar abinci da ayyukan masana'antu da sauya tsarin tattalin arziki ta hanyar samar da kasuwa ta bai daya da za ta ba da damar zirga-zirgar mutane da kayayyaki da jari da hidimomi ba tare da shinge ba.

Shugaban na Sudan ya samu rakiyar Ministan dake kula da fadarsa da Ministan harkokin wajen kasar da babban manajan ofishin shugaban kasa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China