in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci a taimaka wajen ciyar da tsarin siyasar DRC gaba
2018-03-20 09:11:40 cri

Mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Wu Haitao, ya bukaci al'ummomin kasashen duniya su taimaka wajen ciyar da tsarin siyasar jamhuriyar demokradiyyar Congo DRC gaba.

Wu Haitao, ya bayyanawa kwamitin sulhu na MDD a jiya cewa, ya kamata kasashen duniya su ci gaba da aiki don ganin bangarori daban daban na kasar sun cimma maslaha a siyasance ta hanyar tuntuba da tattaunawa, tare da mara baya ga shiga tsakani da kungiyoyin yankin kamar AU da kungiyar raya yankin babban tafki ke yi.

Ya kara da bukatar kasashen duniya su tabbatar da shugabancin gwamnatin kasar wajen warware rikicin, tare da martaba ikon kasar na mallakar yankunanta.

Wu Haitao, ya ce gwamnatin jamhuriyar demokradiyyar Congo ce ke da nauyin kare fararen hula, kuma abun da ya kamata kasashen waje su yi shi ne, taimakawa gwamnatin inganta harkokin tsaro.

Ya ce, har kullum kasar Sin na taimakawa tsarin wanzar da zaman lafiya, tare da shiga harkokin wanzar da zaman lafiya a kasar, har ila yau, ya ce kasar Sin tana ba ta tallafin kayayyakin agaji, kuma tana ba da gudunmuwa wajen inganta zamantakewa da tattalin arzikin kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China