Sanarwar da fadar shugaban kasar Koriya ta Kudu ta fitar a jiya ya ruwaito cewa, kwamitin zai kuma samar da wata tawagar masu bada shawara da za ta kunshi mutane 30 zuwa 40, inda tsohon Ministan harkokin hadin kai na Koriya ta Kudu Lim Dong-won zai shugabanci tawagar, domin kara wa juna sani kan ganawa sau biyu da shugabannin kasashen biyu suka taba yi a baya, tare kuma da tattara shawarwari daga bangarori daban daban. (Maryam)